6 Maris 2021 - 08:18
Isra’ila Tana Kokarin Ganin Hamas Ba Ta Sami Nasara A Zaben Falasdinawa Mai Zuwa Ba

Wasu kafafen yada labarai na Isra’ila sun bayyana cewa gwamnatin yahudawan ta yi barazana ga ‘yan siyasa masu goyon bayan kungiyar Hamas a yankin yamma da kogin Jordan kan cewa kada su kuskura su shiga takarar zaben shuwagabannin Falasdinbawa wadanda za’a gudanar a cikin wannan shekarar.

ABNA24 : Jaridar Ha’arez ta yahudawan ta bayyana cewa hukumar leken asiri ta cikin gida wato ‘Shabok’ ta kira wasu fitattun ‘yan siyasa masu goyon bayan kungiyar Hamas a yankin yamma da kogin Jordan inda ta ja kunnensu kan shiga zabubbukan Falasdinawa masu zuwa.

Labarin ya kara da cewa idan ‘yan siyasa masu goyon bayan Hamsa sun sami nasara a zabubbukan kamar yadda suka yi a shekara ta 2006 to yahudawan zasu dakatar da bawa gwamnatin Falasdinawan kudaden da take basu na haraji da na fito wanda kuma zai zama matsala ga biyan albashin ma’aika.

342/